Isa ga babban shafi
IS-Tunisia

IS ta dauki alhakin kisan Sojin Tunisa 4 a harin bom

Kungiyar IS ta dauki alhakin kisan Sojin Tunisia 4 a wani farmakin bom da aka kai kan tawagar Sojin ranar 3 ga watan da muke ciki na Fabarairu.

Tun bayan hambarar da gwamnatin Zine El Abidine ben Ali Tunisa ke fama da ayyukan ta'addanci.
Tun bayan hambarar da gwamnatin Zine El Abidine ben Ali Tunisa ke fama da ayyukan ta'addanci. Hatem SALHI / AFP
Talla

IS cikin bayanan da ta wallafa a jaridarta ta Al-Naba da ke bayyana yadda ta shirya kisan Sojin 4 ta kuma bayyana yadda ta yiwa Sojin na Tunisia kutse ranar 20 ga watan Disamban bara a sansaninsu na yankin Kasserine da ke gab da tsaunin Selloum.

Wani bayani da sashen fikira na Amurka mai sanya idanu kan ayyukan ta’addanci ya fitar yau Juma’a ya ce Sojojin 4 sun rasa rayukansu bayan tashin bamabamai har guda 3 a yankin da ke gab da tsaunin Mgila na kasar.

Tun a ranar 3 ga watan nan ne ma’aikatar tsaron Tunisia ta sanar da kisan Sojin a kokarinsu na laluben maboyar ‘yan ta’addar da suka yi sansanin a tsaunin na Mgila.

Tunisia dai na kallon Mgila da Chaambi da ke gab da iyakar kasar da Algeria a matsayin maboyar mayakan ta’addanci da ke kai farmakin sari-ka-noke a sassan kasar.

A jawabin Firaminista Hichem Mechichi, ya ce kisan Sojin 4 ba zai sanyaya musu gwiwa game da damarar da suka daura ta kakkabe ayyukan ta’addanci a sassan kasar ba.

Tun bayan juyin juya halin 2011 da ya hambarar da gwamnatin Zine El Abidine ben Ali, Tunisa ke ci gaba da fuskantar tashe-tashen hankula ciki har da hare-haren ta’addanci wanda ya hallaka gomman Sojin kasar musamman a yankin Kasserine da ke matsayin maboyar mayakan AQIM reshen Al-Qaeda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.