Shirin rigakafin Korona ya kan-kama a Afrika
Miliyoyin alluran rigakafin coronavirus da aka samar karkashin shirin Covax, sun isa Najeriya da Jamhuriyar Demokuradiyar Congo da Angola da Kenya, a daidai lokacin da kasashen Afrika ke kara kaimi wajen yi wa jama’arsu rigakafin cutar.
Wallafawa ranar:
Najeriya wadda ke zama kasa mafi yawan al’umma a Afrika, ta karbi allurai kimanin miliyan 4, yayin da Jamhuriyar Demokuradiyar Congo ta karbi miliyan 1.7, inda kuma Angola ta karbi sama da dubu 600, a daidai lokacin da Gambia ke dakon karbar dubu 30.
Nigeria has received 3.92 million doses of the AstraZeneca COVID-19 vaccine through the COVAX initiative. pic.twitter.com/uGP1UAEjcN
— Africa Facts Zone (@AfricaFactsZone) March 2, 2021
Ita ma Kenya ta karbi alluran na AstraZaneca karkashin shirin Covax har guda miliyan 1.
A makon jiya ne Ghana da Ivory Coast suka zama kasashen Afrika na farko da suka fara karbar rigakafin wanda aka samar da shi kyauta ga kasashen duniya matalauta.
Tuni kasashen duniya mawadata suka yi nisa a shirin yi wa al’umominsu rigakafin cutar ta coronavirus, inda suka yi wa kananan kasashe da dama fintinkau, abin da ya sa Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi gargadin cewa, ba za a ci galabar wannan annoba ba har sai kowacce kasa ta yi wa jama’arta rigakafin.
Sai dai har yanzu ana fuskantar kalubalen gudanar da shirin rigakafin a wasu tarin kasashen Afrika saboda matsalar kayayyakin more rayuwa da kuma tabarbarewar tsaro kamar yadda Faisal Shuaib, darekta a Hukumar Kiwon Lafiya ta Najeriya Matakin Farko ya bayyana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu