Isa ga babban shafi

Zaben yan Majalisu zagaye na biyu a Afrika ta Tsakiya

An soma zaben yan majalisu ,zagaye na biyu a Afrika ta Tsakiya, zaben dake tattare da kalubale  sabili da matsallolin tsaro.

Akwatin zabe a makarantar Barthélemy Boganda daya daga cikin manyan makarantu a birnin bangui.
Akwatin zabe a makarantar Barthélemy Boganda daya daga cikin manyan makarantu a birnin bangui. © AFP - Alexis Huguet
Talla

Akala mutane milyan daya ake sa ran za su fito don kada kuri’un su a dai dai lokacin da  majalisar dimkin Duniya ranar juma’a da ta gabata, ta amince da wani shiri na tura karin sojojin ta 3000 da zasu dafawa wajen tabbatar da tsaro a lokacin zaben.

Rahotanni daga bangui babban birnin kasar na nuni cewa gwamnati ta dau matakan tsaro fiye da kima da nufin kare lafiyar jama'a a sassa unguwanin birni ga baki daya.Rasha daga cikin kasashe masu bayar da gundumuwa ta fani tsaro a kasar ,ta bakin mataimakin jakadan kasar a zauren majalisar Dimkin Duniya,ya bukaci Majalisar dimkin Duniya ta kawo karin haske dangane da manufofin da take da su ,har ta dau matakin tura karin sojojin wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.