Al'ummar Mali na zanga-zangar bukatar ficewar Sojin Faransa daga kasar
Wasu Mutane yau sun gudanar da zanga zanga a Bamako da ke kasar Mali inda su ke bukatar ganin sojojin Faransa sun fice daga kasar mai fama da tashe-tashen hakula, kwana guda bayan mutuwar mutane 6 sakamakon harin sojojin Faransar.
Wallafawa ranar:
Rundunar sojin Faransa ta ce ta kai harin ne kan masu fafutukar jihadi a arewa maso gabashin Mali, amma mazauna yankin sun ce matasa ne da ke farauta aka kashe.
Kasar Faransa ta kai wa Mali dauki a shekarar 2013 domin taimakawa gwamnatin kasar kawar da masu fafutukar kafa daula a yankin.
Yanzu haka Faransa na da dakaru 5,100 a yankin Sahel dake aiki a karkashin rundunar Barkhane.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu