Masu corona a Afrika sun zarce miliyan 14
Hukumar da ke yaki da cututtuka ta Afirka ta ce adadin mutanen da suka kamu da cutar korona a fadin nahiyar sun kai miliyan 14 da dubu 187,097, yayin da dubu 111 da 919 suka mutu, yayin da miliyan 3 da dubu 746 da 992 suka warke.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta bayyana kasashen Afirka ta Kudu da Morocco da Tunisa da Masar da kuma Habasha a matsayin wadanda suka fi jin radadin cutar.
Idan aka koma batun shiya-shiya kuma, shiyar kudancin Afirka ke sahun gaba, sai Afirka ta arewa da gabashin Afirka, yayin da cutar ke da sauki a yankin tsakiyar nahiyar.
Ya zuwa yanzu kasashen Afirka sun karbi allurar rigakafin cutar sama da miliyan 26 a karkashin shirin taimaka musu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu