Isa ga babban shafi
DRCongo

Yan Sanda sun harbe mutun daya a garin Butembo

Yan Sanda a garin Butembo na Jamhuriyar Demokkuradiyar Congo sun harbe ha lahira mutun daya a jiya juma’a daga  cikin masu zanga don nuna adawar su dangane da  rashin tabuka ko wani abin a zo a gani daga rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dimkin Duniya.

Wasu daga cikin masu zanga-zanga a garin butembo na kasar  DRCongo
Wasu daga cikin masu zanga-zanga a garin butembo na kasar DRCongo ALEXIS HUGUET / AFP
Talla

Yan Sanda a kokarin su na share  wasu daga cikin shingaye da masu zanga-zanga suka  dasa saman hanyoyi sun fuskanci bore daga masu zanga-zanga,wanda hakan ya kais u ga bude wuta saman su.

Kanal Jean Paul Ngoma shugaban rundunar yan Sanda na garin Butembo ne ya tabbatar da mutuwar mutumen.

Kungiyoyin kare hakokin bil Adam a kasar na ci gaba da kokawa dangane da matakan da yan Sanda ke amfani da su yayin zanga-zangar farraren fula. awasu yankunan kasa ta DRCongo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.