Isa ga babban shafi
Saliyo - Ebola

Saliyo za ta yi wa ma’aikatan lafiyarta dake kan iyakar Guinea rigakafin Ebola

Gwamnatin Saliyo ta sanar da cewa za ta yi wa ma’aikatan kiwon lafiyarta allurar rigakafin cutar Ebola a yankunan da ke kusa da kan iyakarta da Guinea, inda cutar ta sake bulla a watan Janairu.

Zane dangane da rigakafin annobar Ebola
Zane dangane da rigakafin annobar Ebola © Dr Meddy
Talla

Ministan lafiyan kasar Austin Demby ya bayyana haka cikin wata sanarwa,  cewa kamfanin samar da magunguna na Amurka Johnson & Johnson zai basu allurai 640 na rigakafin cutar ta Ebola ranar Asabar da kuma dubu 3,840 a ranar Lahadi a matsayin gudummawa.

Wasu jami'an Lafiya da ke shirin tunkarar aikin rigakafin na Ebola.
Wasu jami'an Lafiya da ke shirin tunkarar aikin rigakafin na Ebola. REUTERS/Baz Ratner/File Photo

Sanarwar ta ce "lura da barkewar cutar Ebola a makwabtan Guinea, ma'aikatan lafiya dake gundumomin kan iyaka na cikin barazanar kamuwa da cutar idan har kwayar ta bazu zuwa Saliyo."

Cutar mai saurin kisa ta sake bayyana a Guinea a cikin watan Janairu, abinda yasa ake daukar makan ganin cutar batayi illa kamar wadda tayi a shekarar 2013 zuwa 2016 a Yammacin Afirka, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 11,300 a Guinea da Liberiya da kuma Saliyo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.