Kotu ta amince da nasarar Talon a zaben Benin
Kotun Fasalta Kundin Tsarin mulki da ke Jamhuriyar Benin ta amince da sakamakon zaben shugaban kasar da aka yi a karshen mako wanda ya bai wa Patrice Talon nasarar samun wa’adi na biyu.
Wallafawa ranar:
Matsayin kotun na zuwa ne jim kadan kafin yi wa abokin takarar shugaban Joel Aivo da aka haramta wa shiga zaben tambayoyi dangane da tashin hankalin da aka samu a kasar.
Shugaban Kotun Joseph Djogbenou ya ce, sun amince da sakamakon na wucen-gadi, inda suka bukaci masu korafi da su gabatar nan da kwanaki 5 masu zuwa.
Hukumar zabe ta bayyana cewar shugaba Talon ya samu sama da kashi 86 na kuri’un da aka kada a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu