Isa ga babban shafi
Saliyo - Hakkin dan Adam

Gwamnatin Saliyo za ta soke dokar hukuncin kisa a kasar

Mataimakin ministan Shari’ar Saliyo Umaru Napoleon Koroma, ya ce gwamnatin kasar za ta soke zartas da hukuncin kisa nan ba da jimawa ba.

Gwamnatin Saliyo na neman soke zartaswa da masu laifi hukuncin kisa.
Gwamnatin Saliyo na neman soke zartaswa da masu laifi hukuncin kisa. © Humanists International
Talla

Ministan ya bayyana matsayar gwamnatin ta Saliyo ne a ranar Laraba, inda ya ce za su mika kudurin gaban majalisar kasar domin tabbatar da sabuwar dokar ta soke zartas da hukuncin kisa kan masu laifi.

Rabon da a zartaswa da wani hukuncin kisa a Saliyo dai tun shekarar 1998, la’akari da cewar ko da kotu ta yanke hukuncin na kisa ana sassauta ta shi ne.

Kawo yanzu dai ba a fayyace ranar da majalisar kasar ta Saliyo za ta yi muhawara kan kudirin sabuwar dokar shugaba Julius Maada Bio ba, wanda ya ce ya dauki matakin ne domin karfafa ‘yan ci tare da kare hakkokin al’ummar kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.