Nijar-Cote d'Ivoire
Wani bidiyon karya ya haddasa rikici a Cote d'Ivoire tare da farwa 'yan Nijar
Mahukuntan kasar Cote d’ivoire sun tabbatar da cewa yanzu haka ana tsare da mutane 12 bayan rikicin da ya faru wanda zauna gari banza suka afka wa ‘yan asalin jamhuriyar Nijar da ke zaune a Abidjan babban birnin Kasar.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:39
Talla
Rikicin dai ya barke ne bayan da aka yada wani hoton bidiyo da aka bayyana cewa jami’an tsaron Nijar ne ke cin zarafin ‘yan kasar ta Cote d’ivoire da ke kasar ta Nijar a kan hanyarsu ta zuwa Turai, bidiyon da aka bayyana cewa karya ce.
Ga rahoton da wakilinmu da Salisu Isa ya aiko mana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu