Dan Ghaddafi ya bayyana aniyar takarar shugaban Libya
Saif al-Islam, dan shugaban kasar Libya Muammar Gaddafi da aka kashe a shekarar 2011 ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar, tare da maido da hadin kanta, bayan yakin da aka shafe shekaru 10 ana yi ya wargaza ta.
Wallafawa ranar:
Ya bayyana haka ne wata ganawa da ya yi da jaridar ‘New York Times’ a gidansa da ke garin Zintan, yammacin kasar da ke arewacin Afrika.
Dan shekaru 49 din, wanda kafin shekarar 2011 ake mai kallon wanda zai gaji mahaifinsa ya ce a cikin shekaru 10 da suka wuce, babu abin da ‘yan siyasa suka tsinana wa kasar face ukuba da tashin hankali, yana mai cewa lokaci ya yi da za a koma yadda ake a da.
An shafe shekaru ba tare da an san inda al-Islam, wanda kotun hukunta laifukan yaki ke nema ruwa jallo ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu