Isa ga babban shafi
MOZAMBIQUE-MALAWI-MADAGASCAR

Guguwar Ana, ta kashe mutane sama da 70 a Mozambique, Malawi da Madagascar.

Adadin mutanen da suka mutu sakamakon mahaukaciyar guguwar Ana, da ta haddasa ambaliyar ruwa a kasashen Mozambique, Malawi da Madagascar sun kai 70.A cewar hukumomin kasashen, adadin ka iya karuwa kasancewar har yanzu ana ci gaba da aikin ceto da nufin gano wasu karin mutanen.

Hoton Guguwar Ana
Hoton Guguwar Ana © Wikicommons
Talla

Hukumomi  da  masu  aikin  ceto  na  cigaba  da  kokarin  gano  musababin faruwar hakan a  kasashen  uku  da  kuma  taimaka  wa  wanda  suka  jikata.

Wannan dai na zuwa ne bayan da makeken kogi ya yi awon gaba  da wasu jami’ai da gwamnatin kasar ta aika don tattaron bayani a game da bannar da guguwar da kuma ambaliyar ruwan suka haddasa.

A rahoton da Madagaskar   ta  fitar  ta ce mutane  41  sun  cimma  ajalinsu a yayin da 18 suka mutu a Mozambik, sai guda 11  da suka rasa rayukan su a   kasar  Malawi.

Lamarin  a  Madagaskar   ya  sanya   daruruwan mutane  barin gidajensu,  abinda ya sanya  makarantu  da  wuraren  motsa jiki  suka  zama  sansanin gudun hijira.

Ko a Mozambique ma haka lamarin yake, don kuwa tuni gwamnatin kasar ta  ce, a yanzu tana mayar da hankali ne wajen gyara turakun wutar lantarki da guguwar ta lalata, da nufin baiwa asibitoci lantarki don kulawa da marasa lafiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.