Isa ga babban shafi
DR Congo

Harin 'yan tawaye ya yi sanadin mutuwar mutane 12 a Congo

Akalla fararen hula 11 galibi tsoffi da kuma soji guda aka kashe sakamakon wani harin da 'yan tawaye suka kai a lardin Ituri da ke arewa maso gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Wasu dakarun Jamhuriyar Dimokardiyyar Congo a yanki Ituri.
Wasu dakarun Jamhuriyar Dimokardiyyar Congo a yanki Ituri. REUTERS
Talla

Wani jami'in yankin Gedeon Dino ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar, "yan ta'addar CODECO sun kai hari kauyen Tshotsho da daren Laraba zuwa safiyar Alhamis, inda suka kashe fararen hula 11 da adduna da bindigu – ciki harda mata da tsoffi.

Kauyen  Tshotsho yana da nisan kilomita 30 ne daga ainihin lardin Ituri na garin Bunia.

Kungiyar  Codeco dai wata shu’umar kungiyar kabila ce ta masu dauke da makamai da ke ikirarin kare muradan ‘yan kabilar Lendu.

kabilun  Lendu da Hema  sun dade suna kai ruwa rana da juna, lamarin da ya kai da sarar rayuka. tsakanin shekarun 1999 zuwa 2003 kafin dakarun kiyaye zaman lafiya na Turai su shiga tsakani.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.