Isa ga babban shafi

An kashe mutane 20 a harin Congo

Akalla mutane 20 ne aka kashe a wani sabon tashin hankali da ya auku a lardin Ituri da ke gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, abin da ake zargin mayakan ADF da suka yi kaurin-suna ne suka kaddamar da harin.

Wasu sojoji a yankin Ituri
Wasu sojoji a yankin Ituri MONUSCO/Force
Talla

An kai harin ne cikin dare a kauyen Bwanasura da ke yankin Irumu, kamar yadda hukumomi a yankin Kivu suka bayyana a shafin Twitter.

Ituri da lardin Kivu ta Arewa na fama da hare-haren kungiyoyin masu dauke da makamai, wadanda yawancinsu suka yada zango a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango.

Hukumar Tsaron Kasar ta ce ana zargin kungiyar ADF da ke ikrarin jihadi da alhakin kai harin.

Ko da yake an kai wa ADF hari a wani farmakin hadin gwiwa da dakarun gwamnati da na Uganda suka kaddamar a watan Nuwambar bara bayan hare-haren bama-bamai a Kampala babban birnin kasar ta Uganda.

A cikin watan Maris, akalla mutane 30 ne ake zargin 'yan tawayen suka kashe a Arewacin Kivu sannan sama da mutane 50 ne suka mutu a wani hari na kwanaki biyu da suka kai kauyukan Irumu.

Ana zargin kungiyar ADF da aikata kisan kiyashi, sace-sace, inda aka yi kiyasta adadin rayukan da ta kashe ya kai dubbai a kasar.

Tun daga watan Afrilun 2019, wasu hare-haren da aka kaddamar a gabashin kasar, ADF ta dauki alhakin kaiwa, kuma tuni kungiyar IS, ta bayyana kungiyar a matsayin reshenta da ke yankin tsakiyar Afirka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.