Isa ga babban shafi

Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 20 a Jamhuriyar Nijar

Hukumomi a Jamhuriyar sun gargadi al'ummar kasar da su kara taka tsan-tsan, yayin da ambaliyar ruwa ta yi sanadin rayuwakn mutum 20, inda wasu 27 suka jikkata.

Ambaliyar ruwa na ci gaba da yin barna a sassa da dama na nahiyar Afirka
Ambaliyar ruwa na ci gaba da yin barna a sassa da dama na nahiyar Afirka © guardian.ng
Talla

Hukumomin bada agajin gaggawa sun ce daga lokacin da aka fara samun saukar ruwan sama a wannan shekara an samu asarar tarin dukiyoyi, baya ga asarar rayuka da dama.

Wannan na zuwa ne yayin da masu rajin kare muhalli ke gargadin gwamnatocin kasashe, kan illolin da ke tattare da matsalar sauyin yanayi, ciki kuwa har da ambaliyar ruwa, wanda tuni aka fara ganin hakan a kasashe da dama.

Alkalumman da mahukunta suka fitar a Jamhuriyar Nijar, sun ce ambaliyar ta bana, kawo yanzu ta shafi mutane sama da dubu 48, yayin da daruruwan dabbobi suka mutu, kamar dai yadda ambaliyar ta shafi makarantu, wuraren ibada, da kuma rumbuna ajiye abinci a sassa da dama na kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.