Isa ga babban shafi

Hukumar zaben Senegal ta shiryawa zaben yan majalisu na gobe lahadi

An kawo karshen yakin zaben yan majalisu na kasar Senegal, zaben da za a yi gobe lahadi 31 ga watan  yuli a wani lokaci da yan siyasa musaman bangaren adawa ke kokawa  ganin yada shugaban kasar Macky Sall ke tafiyar da shugabanci.

Shugaban kasar Senegal Macky Sall.
Shugaban kasar Senegal Macky Sall. © RFI
Talla

Kujeru 165 ne yan siyasar kasar  daga jam'iyyu takwas za su nemi lashe wa.

Zaben dake a matsayin zakaren gwajin dafi ga Shugaban kasar Macky Sall,da tarin yan kasar ke kallon sa a matsayin wanda ya gaza wajen magance matsallolin da suka hada da tsadar rayuwa,rugujewar inci fada  aji.

Yan siyasa bangaren  adawa sun shirya kam a wannan zabe na ganin sun samu rijaye a zauren majalisar,wata hanyar tilastawa shugaban  kasar canza salon siyasa da kuma damawa da yan adawa a shugabancin kasar ta Senegal.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.