Isa ga babban shafi

Bayan da Mali ta sallame su, sojojin Cote d'Ivoire 46 sun koma gida

Bayan da shugaban Mali Assimi Goita ya yi musu afuwa,  sojoji 46 ‘yan asalin kasarcote d’Ivoire wadanda aka yanke wa hukuncin dauri a gidan yari, sun isa birnin Abidjan a yammacin jiya asabar.

Jirgi dauke da sojojin Cote'Divoire 46 lokacin da ya isa Abidjan ranar 7 ga watan Janairun 2023.
Jirgi dauke da sojojin Cote'Divoire 46 lokacin da ya isa Abidjan ranar 7 ga watan Janairun 2023. © https://www.facebook.com/Presidencecotedivoire
Talla

Sojojin dai sun share tsawon watanni 6 tsare a hannun mahukuntan kasar Mali, bayan da aka bayyana cewa sun shiga kasar ne a matsayin sojin haya, yayin da daga bisani kotu ta yi zama tare da yanke musu hukuncin daurin shekaru 20 kowanne tare da biyan tare da ta kudi cfa milyan biyu.

Wata majiya ta ce, kafin isa birnin Abidjan, sojojin sun yada zango a kasar Togo domin ganawa da shugaba Faure Gnasingbe wanda ya shiga tsakanin domin warware wannan takaddama tsakanin Mali da Cote d’Ivoire.

Yayin da isarsu a birnin Abidjan kuwa, shugaba Alassan Ouattara ya gana da sojojin, tare da jinjina wa kokarin da kasashe aminai suka yi domin ‘yantar da wadannan sojoji. Hakazalika, Ouattara a jawabin nasa, ya bayyana Mali a matsayin kasa aminiya ga Cote d’Ivoire.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.