Isa ga babban shafi

Prime ministan Mali ya dakatar da ziyara a arewacin kasar saboda matsalar tsaro

Prime ministan Mali Choguel Kokalla Maiga ya dakatar da ziyarar sa a yankin arewacin kasar sakamakon barazanar matsalolin tsaro.

Taswirar garuruwan da aka shirya zuwan Prime ministan Mali
Taswirar garuruwan da aka shirya zuwan Prime ministan Mali AFP
Talla

Maiga mai shekaru 64 ya isa birnin Gao a ranar juma’ar da ta gabata a ziyarar aiki ta kwanaki 4, yayin da cikin ziyarar aka tsara zai ziyarci garuruwan Bourem da Ansongo.

A yanzu dai an dakatar da ziyarar garuruwan biyu, saboda rahotannin ta’azzarar hare-haren ‘yan ta’adda, kamar yadda guda daga cikin kusoshin gwamnatin kasar ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa AFP.

Magajin garin Bourem Hamadou Mahammane Toure ya tabbatarwa da manema labarai soke ziyarar, wadda ke zama karon farko da Prime ministan ya kai arewacin kasar tun watan Disamba, bayan fama da cutar shanyewar barin jiki.

A yayin ziyarar dai an shirya Maiga zai tattauna da shugabannin al’umma da sojojin dake bakin daga, sannan kuma zai rabawa manoma kayayyakin aikin gona da nufin rage musu radadin ayyukan ta’addancin, yayin da zai kaddamar da wasu ayyukan ci gaba a yankunan, wadanda gwamnati ta samar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.