Isa ga babban shafi

An kashe fararen hula 40 a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo

Sama da mutaane 40 ne aka kashe a wasu hare  hare da aka kai wasu kauyuka a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo  a jiya Juma’a, kamar yadda wasu majiyoyi a yankunan suka bayyana, inda suke zargin  ‘yan tsagerar  kungiyar CODECO  da wannan aika aika.

Wani kwamandan kungiyar CODECO  yankin Ituri na Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.
Wani kwamandan kungiyar CODECO yankin Ituri na Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo. AFP - ALEXIS HUGUET
Talla

Ana zargin kungiyar ta CODECO da kai hare hare a akalla kauyuka 3 a lardin Ituri,  mai kimanin nisan kilomitaa 60 daga shelkwatar lardin, Bunia.

CODECO, na daya daga cikin dimbim kungiyoyi masu dauke da makamai da ke cin karensu babu babbaka a yankin da ke da arzikin albarkatun kasa a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Kungiyar tana ikirarin rajin kare ‘yan kabilar Lendu daga hare haren ‘yan kabilar Hema da  kuma sojoji.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.