Isa ga babban shafi

Rikicin Sudan: Sama da mutane dubu 20 suka tsallaka zuwa Chadi

Hukumar abinci ta duniya ta ce hukumomin Chadi hade da kungiyoyin agaji na bukatar tallafin gaggawa domin taimakawa dubban masu gudun hijira dake tsallakawa daga sudan dake makotaka da kasar.

Wasu 'yan gudun hijira da suka tsere daga rikici
Wasu 'yan gudun hijira da suka tsere daga rikici REUTERS/Stringer/File photo
Talla

Majalisar dinkin duniya ta ce akalla mutane dubu 20 ne suka tsallaka Sudan zuwa Chadi tun bayan barkewar  rikici tsakanin rundunar sojin kasar da dakarun kai daukin gaggawa a farkon watan nan na Afrilu.

Darektan hukumar a Chadi, Pierre Honnorat na cewa bukatar ta yi tsanani sosai domin nan da makonni 6 ko 8 masu zuwa ba za su iya kai wa yankunan da masu gudun hijirar suke dauki ba saboda yanayi na ruwan sama.

Tun a farkon makon nan aka soma rabawa ‘yan gudun hijiran da suka isa kan iyakar Adre abinci da sauran kayakin jinkai.

 

Rikicin da aka shafe sama da makonni 2 ana yi ya mayar da Khartoum tamkar filin daga, sannan ya jefa illahirin Kasar cikin halin kaka-ni-kayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.