Isa ga babban shafi

Sonko ya bukaci 'yan Senegal su gudanar da gangami gabani jawabin shugaba Sall

Jagoran ‘yan adawar Senegal Ousmane Sonko, ya bukaci al’ummar kasar su fito don yin gangami, a dai-dai lokacin da ake saran shugaban kasar Macky Sall, zai gabatar da jawabin ko zai sake neman wa’adi na uku.

Jagoran 'yan adawar Senegal Ousmane Sonko.
Jagoran 'yan adawar Senegal Ousmane Sonko. © AFP - MUHAMADOU BITTAYE
Talla

Sonko ya ce lokaci ya yi da za su nuna wa Sall bayada hurumin kakabawa al’umma ‘yan takara a zaben shugaban kasar da ke tafe.

A farkon watan Yunin da ya gabata ne, aka yankewa Sonko hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari, bayan samunsa da laifin yin lalata da wata, lamarin da ya haifar da zanga-zangar da tayi sanadin mutuwar mutane 16.

Wannan hukuncin dai, ya haramta masa tsayawa takarar shugabancin kasar a zaben da za’a yi shekara mai zuwa, wanda Sonko ya ce gwamnatin kasar ce ta kitsa hakan, zargin da tuni ita kuma ta karyata.

Da misalin karfe 8 na daren yau Litinin agogon kasar ne, ake saran shugaba Sall ya bayyana matsayarsa ta ko zai tsaya takarar shugabancin kasar a karo na uku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.