Isa ga babban shafi

Tunisia ta dakatar da albashin malamai sama da dubu 17, saboda matsin tattalin arziki

Mahukunta a Tunusia sun dakatar da biyan albashin malaman makaranta dubu 17 tare da korar wasu shugabanin makarantu 350, matakin da ke zuwa a wani yanayi da matsalolin tattalin arziki suka dabaibaye kasar ta arewacin Afrika. 

Le président Kaïs Saïed, à Carthage, le 27 février 2020.
Le président Kaïs Saïed, à Carthage, le 27 février 2020. REUTERS - POOL New
Talla

Wannan mataki na gwamnati dai ya shafi akalla kaso 1 bisa 3 na daukacin malaman makarantu da ke Tunisia wanda kuma ake ganin zai sake zafafa kakkarfar zanga-zangar da bangaren ilimi ke ci gaba yi, da ke ganin na daga cikin dalilan da suka sanya gwamnati aiwatar da wannan hukunci. 

Malaman makarantu a Tunisa dai sun yi tsayuwar gwamen jaki wajen kin gudanar da aikin baiwa dalibai maki a jarabawar da dalibai suka kammala a a baya-bayan nan. 

Cikin dalilan da gwamnatin ta Tunisia ta bayar, sun hadar da mummunan koma bayan da tattalin arzikin kasar ke fuskanta, da ya tilasta gaza iya daukar nauyin malaman. 

Tunisia dai na sahun kasashen da ke ganin mummunar tabarbarewar tattalin arziki da hauhawar farashin kayaki sai kuma kamfar abinci baya ga karuwar marasa aikin yi.. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.