Isa ga babban shafi

Hukumar (Céni) ta tsawaita da mako guda wa'adin mika takardun takara a DRC

A Jamhuriyar,Demokradiyyar Congo hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (Céni) ta tsawaita da mako guda wa'adin mika takardun tsayawa takara ga mataimakin na kasa a babban zaben da za a gudanar a ranar 20 ga watan Disamba, 2023.

Zauren hukumar zaben DRCongo
Zauren hukumar zaben DRCongo © John Wessels - AFP
Talla

 

A hukumance a jiya asabar ne ya kamata a kawo karshen karbar  sunayen yan takara daga hukumar  zaben Jamhuriyar,Demokradiyyar Congo.

Dénis Kadima, Shugaban hukumar zabe ta CENI a DRCongo
Dénis Kadima, Shugaban hukumar zabe ta CENI a DRCongo © CENI DRC

A karshe dai  ofishin hukumar zaben zai ci gaba da kasancewa a bude har zuwa ranar Lahadi 23 ga watan Yulin nan 2023. Duk da cewa a kwanakin baya, shugaban hukumar ta CENI, Denis Kadima, ya yi gargadi karara cewa ba za a yi wani karin wa'adi ba. A ƙarshe, an ba da ƙarin kwanaki bakwai ga 'yan takara na gaba.

Sanarwar da Hukumar zaben kasar na zuwa a wani lokaci da 'yan adawa ke bayyana damuwarsu biyo bayan kisan wani dan majalisa bangaren Moise Katumbi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.