Akalla mutane 23 ne suka mutu sakamakon zaftarewar kasa a Yaoundé
A kasar Kamaru ,akalla mutane 23 ne suka mutu sakamakon zaftarewar biyo bayan shatata ruwan sama da aka yi a yammacin jiya Lahadi a birnin Yaoundé, babban birnin kasar ta Kamaru.
Wallafawa ranar:
Birnin na Yaounde na daga cikin yankunan da ake fuskantar rushewar gidaje jeyi-jeyi a duk lokacin da aka tunkarin,ganin ta yada birnin yake zagaye da tsaunuka da gangara ba tare da an ayi aiki da tsari gina gidaje yada ta kamata.
Iftil’ain da ya faru a gundumar Mbankolo, da ke wajen arewa maso yammacin birnin Yaoundé, kuma ya faru ne sakamakon fashewar wata madatsar ruwa a wani tafki na wucin gadi kmamar dai yada kafafen yada labaren kasar suka ruwaito.
A bangaren hukumar kashe gobira ta kasa, Shugaban hukumar David Petatoa Poufong ya shaidawa manema labarai a safiyar yau litinin cewa ma’aikatan hukumar sun samu nasarar zakulo gawarwakin mutane 15 a jiya kuma da safiyar yau litinin sun gano wasu matatun 8.
Wani Jami’in kwana-kwana a wurin da al’amarin ya faru ya bayyana cewa daga cikin mutanen da suka rasa rayukan su akwai yaro daya.
Jami’an tsaro na kokarin nisanta farraren daga ainihin wurin da zaizayar kasa ta afku tare da dasa shingen tsaro.
Gani girman wannan barna kasasncewa ruwan sun kwashe duk wani abu da ke kan hanyarsu, Daouda Ousmanou, shugaban sashin II na Yaoundé inda Mbankolo yake, ya isar da kira ga jama’a na su yi hatara wajen gina gidaje.
A ranar 27 ga Nuwamba, 2022, akalla mutane 15 ne suka mutu sakamakon zaftarewar kasa a wani yanki na tudu da ke gundumar Damascus, kudancin Mbankolo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu