Isa ga babban shafi

'Yan adawan Chadi sun zargi gwamnati da yi wa jagoransu kisan gilla

Babbar jam’iyyar adawa a Chadi ta zargi gwamnatin sojin kasar da kisan jagoranta a wani samame da dakarun kasar suka kai shelkwatarta gabanin zaben da ke tafe a watan Mayun wannan shekarar.

 Yaya Dillo jagoran 'yan adawar Chadi, wanda ya gamu da ajalinsa a ranar Larabar da ta gabata.
Yaya Dillo jagoran 'yan adawar Chadi, wanda ya gamu da ajalinsa a ranar Larabar da ta gabata. AFP - ISSOUF SANOGO
Talla

Yaya Dillo Djerou shine babban abokin hamayya, kuma dan uwa ga shugaba Mahamat Idriss Deby Itno, wanda ya dare karagar mulki a shekarar 2021  bayan mutuwar mahaifinsa.

Dillo ya mutu ne a ranar Laraba, bayan da sojoji suka yi wa shelkwatar jam’iyyarsa ta Socialist Party Without Borders a babban birnin kasar, N'Djamena, amma gwamnati ta  musanta hannu a kisan nasa.

Wannan na zuwa ne bayan da jagororin mulkin sojin Chadi suka sanar da cewa za a gudanar da babban zaben kasar a ranar 6  ga watan Mayu.

Zaben zai kawo karshen shekaru 3 na gwamnatin rikon kwarya, da zummar maido da aiki da kundin tsarin mulki wajen jagorancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.