Isa ga babban shafi

Anyi gangamin sharar makabartar wadanda suka mutu da cutar Ebola a Liberia

Dumbin mutane sun yi gangamin share kaburbura a makabartar da aka shimfide wadanda cutar Ebola ta kashe mafi girma a Laberiya a ranar Laraba, yayin da kasar ke gab da cika shekaru 10 da fuskantar iftila’in cutar.

Likitocidauke da gawar wadda cutar Ebola ta kashe
Likitocidauke da gawar wadda cutar Ebola ta kashe AFP/John Wessels
Talla

 

Kasar da ke yammacin Afirka ta yi fama da cutar Ebola ce wacce ta barke a tsakanin shekarar 2014 zuwa 2016, ta kuma kashe mutane 4,810 a Laberiya kadai.

An tabbatar da bullar cutar ta farko a kasar ce a ranar 30 ga Maris, 2014, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya.

Fasto Charles Brown, wanda ya kafa gidan marayu ga yaran da iyayensu suka mutu a lokacin cutar Ebola ya ce "Yana da matukar wahala a gare mu.

Makabartar Disco Hill da ke kudu da Monrovia babban birnin kasar an yi ta ne da farko don daukar wadanda cutar Ebola ta kashe, amma a yanzu haka tana dauke da gawarwakin wadanda suka mutu yayin barkewar cutar ta Covid-19.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.