Isa ga babban shafi
Syria

Gwamnatin Syria zata baiwa Talakawa Kudade

Hukumomi a kasar Syria sun sanar da bada tallafin kudade da suka kai Dalan Amirka miliyan 250  ga marasa karfi kimanin 420,000 dake kasar.Ministan Kula da jin dadin jama'a da Kodago na kasar Diala Haj-Aref ya fadawa manema labarai yau cewa matakin na daga cikin matakan da Gwamnatin kasar ta dauka domin ganin an taimakawa magidanta su kasance sun sami abin hannun su.Tallafin inji Ministan sun hada da rancen kudade daga watan gobe.Kamar yadda Fira Ministan kasar mai kulada harkokin tattalin arzikin, Abdallah Dardari ke cewa kashi 14% na alummar kasar miliyan 22 suna fama da talauci.Gwamnatin kasar Syrian ta kuma bayyana cewa zata sarrafa wasu kudade da suka kai Dolan Amirka biliyan 14 wajen wasu ayyukan cigada  nan da shekaru biyar.  

Shugaban kasar Syrian  al-Assad ke shan hannu da sarki Abdallah na Saudiyya a birnin Damascus.
Shugaban kasar Syrian al-Assad ke shan hannu da sarki Abdallah na Saudiyya a birnin Damascus. rfi
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.