Kasashen Larabawa
Kasashen Larabawa zasu goyi bayan Palasdinu
Ministocin Kungiyar kasashen Larabawa, sun bayyana shirin goyawa Palasdinawa baya, wajen samun amincewa da kasarsu a zauren Majalisar Dinkin Duniya, duk da adawar da kasar Amurka ke yi da shirin.Sakataren kungiyar kasashen Larabawa, Nabil al Arabi, yace zasu ci gaba da neman goyan bayan kasashen duniya kan bukatar.Kafin dai taron shugaba Mahmud Abass ya gana da Prime Ministan Turkiya, Recep Tayip Erdogan, daya daga cikin masu goyan bayan kasar ta Palasdinu madugun adawar kasar Isra’ila.
Wallafawa ranar: