Isa ga babban shafi
Syria

MDD ta ce mutane 7,500 sun hallaka cikin rikicin kasar Syria

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa, yanzu haka an kashe mutane 7,500 a ci gaba da tashin hankalin da ake a kasar Syria.Kasar Faransa ta bukaci Rasha da China da su goyi bayan kudirin kawo karshen zub da jinin, da kuma kai kayan agaji ga mabukata, yayin da kasashen biyu ke bayyana bacin ransu kan sukar da Amurka ke musu kan Syrian. 

REUTERS/Stringer
Talla

Tuni kasar ta Amurka na rubuta wani sabon daftari dan mikawa Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, domin barin kai kayan agaji zuwa Syria, inda dubban mutane ke bukata.

Wannan zai zama karo na uku da kasashen Yammacin Duniya ke gabatar da irin wannan kudiri, wanda Rasha da China ke hawa kujerar naki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.