Al’ummar Japan suna bukin tuna bala’in Hiroshima
Dubban mutane ne a kasar Japan suka fito domin juyayin harin da aka kai na atomic bomb a Hiroshima da ke kasar Japan, abinda ya hallaka mutane sama da 140,000 a karshen yakin duniya na biyu.
Wallafawa ranar:
Wadanda suka tsira da ransu da ‘Yan uwan mamatan da suka mutu da Jami’an tsaro da jekadun kasashen Duniya ne suka kai ziyara Hiroshima.
Da misalin karfe 8:15 agogon kasar Japan ne, Ba’amurke, Enola Gay ya jefa bom a ranar 6 ga watan Agusta shekarar 1945.
Jakadan Majalisar Dinkin Duniya a bikin, Angela Kane, ta karanta sakon Ban Ki Moon, tana mai cewa a wannan rana, ba su fatar sake ganin irin wanna lokaci da za’a sake kai harin nukiliya a Hiroshima.
An kiyasta kimanin mutane 5,000 ne suka gudanar bukin, wasu dubun dubatar mutane kuma suka bi zanga-zanga a wajajen ibada da sassan yankunan kasar domin adawa da mallakar makaman Nukiliya a duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu