Isa ga babban shafi
Syria

Mutane 60 sun mutu a harin Syria

Wani harin sama da sojan gwamnatin kasar Syria suka kai a wani gidan burodi, yayi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 60 tare da raunata wasu 50. Shaidun gani da ido sun ce sun ga gawarwaki warwatse a kan tituna, yayin da aka ga wasu cikin gine-ginen da suka rushe.  

Wani gini da Dakarun Syria suka kai hari akansa
Wani gini da Dakarun Syria suka kai hari akansa REUTERS/Kenan Al-Derani
Talla

Harin na yankin Halfaya da ke tsakiyar lardin Hama na zuwa ne a daidai lokacin da mai shiga tsakani na Majalisar Dinkin Duniya, Lakhdar Brahimi, ya fara wani yunkurin kawo karshen rikicin kasar, da ya doshi shekaru 2.
 

Tawaggar masu sa ido kan rikicin ta ce, wadanda suka sami raunuka sakamakon harin na cikin halin mutu ko-koi-rai-ko-koi, kuma akwai yiwuwar mamatan za su karu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.