Isa ga babban shafi
Isra'ila-Felesdinu

Isra’ila za ta saki Falesdinawa 26 'Yan Gidan Yari

Gwamnatin Isra’ila ta ce za ta saki Karin wasu Falastinawa 26 wadanda suka fi dadewa tsare a gidajen yarinta, wannan kuwa domin sauwaka tattaunawar sulhun da za a ci gaba da yi tsakanin bangarorin biyu a jibi Laraba.

Wasu Yahudawa dauke da Hotunan 'Yan uwansu da suke ikirarin Falasdinawa sun kashe
Wasu Yahudawa dauke da Hotunan 'Yan uwansu da suke ikirarin Falasdinawa sun kashe RFI / Nicolas Falez
Talla

Wata sanarwa da hukumomin kasar suka fitar, ta bayyana cewa wadanda za a saka, suna daga cikin jerin fursunoni 104 dukkaninsu Falsdinawa da kuma Larabawan Isra’ila wadanda aka cafke tun kafin kulla yarjejeniyar Oslo ta shekarar 1993.

A gobe Talata ne ake sa ran sakin Falesdinawan, kuma wannan sanarwar na zuwa ne bayan shugabannin Falesdinawa sun zargi Isra’ila da kokarin yin zagon kasa ga yunkurin samun sulhu bayan Isra’ila ta fitar da sanarwar ci gaba da gina wasu sabbin matsugunin Yahudawa a yankunan da ta mamaye.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.