Isa ga babban shafi
Myanmar

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi a sulhu a rikicin kasar Myanmar

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci hukumomin kasar Myanmar da su buda tattaunawa domin shawo kan sabanin da ake fama da shi tsakanin musulmi da kuma mabiyar addinin Buddha na kasar, wadanda sakamakon rikicin da suke yi da junansu aka samu asarar rayukan mutane da dama a cikin shekarar bana.

Rikicin addinin a kasar Myanmar.
Rikicin addinin a kasar Myanmar. Reuters
Talla

Kiran na MDD dai ya zo ne bayan da wasu rahotanni ke cewa an samu barkewar tashin hankali tsakanin musulmi ‘yan kabilar Rohingya da kuma ‘yan Buddha, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutum daya da kuma raunata wasu 10.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.