Isa ga babban shafi
Fransa-Izraila-palestinawa

Fransa ba zata yarda kasar Iran ta mallaki makamin Nukliya ba

Shugaban Faransa wanda ke gabatar da jawabi a gaban Majalisar dokokin Isra’ila a yammacin jiya, ya ce Faransa ba za ta amince da cire wa kasar Iran takunkuman karya tattalin arziki da aka kakaba ma ta ba, sai zuwa lokacin da kasar ta dakatar da shirinta na nukilya.

Le président français François Hollande et le Premier ministre israélien, Benyamin Netanyahu le 17/11/13 lors d'une conférence de presse commune.
Le président français François Hollande et le Premier ministre israélien, Benyamin Netanyahu le 17/11/13 lors d'une conférence de presse commune. REUTERS/Alain Jocard
Talla

Jawabin shugaban kasar ta Faransa dai, ya mayar da hankali ne kan batutuwa da dama da suka hada da batun nukiliyar kasar ta Iran, inda yake cewa, Faransa na nan akan bakantata, kuma ba za ta taba ja da baya dangane da wannan matsayi nata ba.
Hollande ya ce, Faransa ba za ta bar Iran ta mallaki fasahar kera makamin nukiliya ba, kuma ta hanyar tsaurara takunkuman da ke kan kasar ne, za a iya hanata samun irin wannan makamin.

A wani bangare na jawabin nasa kuwa, Francois Hollande ya ce akwai bukatar Isra’ila da kuma Palastinu su ci gaba da tattaunawa domin warware batun gina matsugunan Yahudawa, wanda ke neman yi wa shirin zaman lafiya a tsakaninsu kafar angulu.
To sai dai Hollande ya ce, yana goyon bayan ganin birnin Quds ko kuma Jerusalem, ya ci gaba da kasancewa fadar gwamnatocin Isra’ila da kuma Palastinu, wanda a’l’ummomin biyu za su rayu cikin kwancinyar hankali a tsakaninsu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.