Isa ga babban shafi
Philippines

Guguwar Rammasun ta yi ta’adi a Philippines

Mutane 38 aka tababtar da mutuwarsu a kasar Philippines sakamakon guguwa mai tafe da iska da ruwan saman da ta mamaye kasar tare da katse wutar lantarki. Guguwar ta yi ta’adi a Manila babban birnin kasar da wasu kauyuka.

Wani ma'aikaci rike da da zarto yana kokarin yanka itaciya da ta fadawa mota saboda guguwar Rammasun a Manila kasar Philipphines
Wani ma'aikaci rike da da zarto yana kokarin yanka itaciya da ta fadawa mota saboda guguwar Rammasun a Manila kasar Philipphines REUTERS/Mark DeMayo
Talla

Kafin isowar guguwar gwamnatin kasar ta kwashe mutane sama da 400,000 don tsirar da su.

Kungiyar agaji ta Red Cross tace guguwar ta tafi da rufin gidaje da turakan lantarki tare da lalata dukiya da dama abinda ya yi sanadiyar rasa wutar lantarki ga daukacin mutane miliyan 12 da ke Manila.

Guguwar ta sa an rufe makarantu da ofisoshin gwamnati da kuma kasuwar hada hadar hannayen jari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.