Amurka ta rufe Ofishin jakadancinta na Saudiyya
Kasar Amurka ta rufe Ofishin jakadancinta da ke a Saudi Arebia har na tsawon kwanaki 2 saboda abinda ta kira fargabar matsalar tsaro, bayan wata barazana da aka ce an yiwa ma’aikatan Mai na yankin yammacin kasar
Wallafawa ranar:
Sakamakon matsalar tsaro da ake kasar Amurka ke hange a kasar Saudi Arebiya, hukumomi a kasar Amurka sun sanar da janye ma’aikatansu na Ofishin jakadancinsu da ke a Saudi Arebiya, tare da rufe ofisoshin na kwanaki Biyu.
Ya zuwa yanzu dai Amurkar ta dakatar da dukkanin ayyukan jakadanci tsakaninta da Saudi Arebiya na kwanakin Lahadi da Litinin a Jeddah da Dhahran, tana kira ga jami’anta na Diplomasiyya da su kula da kansu.
Dama dai Ofishin jakadancin kasar Amurka a Saudi Arebiya ya bayyana cewar ma’aikatan Mai nakasashen yammaci na fuskanta a Saudiyya da manufar kai masu hari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu