Afghanistan ta caccaki Pakistan a kan harin Kabul
Shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani ya caccaki Pakistan mai makwabta da kasar ta shi, kan hare-haren da aka kai birnin Kabul a ‘yan kwanakin nan da suka hallaka kusan mutane 60.
Wallafawa ranar:
Shugaba Ghani, ya ce abubuwan da suka faru a ‘yan kwanakin nan, sun nuna cewa har yanzu akwai sansanonin ‘yan kunar bakin wake da wurare kera bama-bamai a kasar ta Pakistan.
Ya ce Afghanistan na fatan samar da zaman lafiya, amma kuma tana karbar sakonnin yaki daga pakistan.
Tun bayan fara jan ragamar mulkin kasar a shekarar da ta gabata shugaba Ghani ke yawan sokar Pakistan kan goyawa ‘yan Taliban baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu