Isa ga babban shafi
Masar

Al-sisi ya amince da murabus din Majalisar Ministocin Masar

Shugaban Kasar Masar Abdel Fatah Al-Sisi ya amince da murabus din Majalisar Ministocin gwamantin Kasar karkashin Firai Minista Ibrahim Mehleb.

Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi.
Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi. REUTERS/Amr Abdallah Dalsh
Talla

To sai dai Shugaba Al-Sisi ya umarci Ministocin da su ci gaba da rike mukamansu kafin a a kafa sabuwar Majalisar Ministocin Kasar.

Wata sanarwa data fito daga fadar shugaban Kasar bata yi karin bayani ba kan dalilin yin murabus din,amma dai  hakan na zuwa ne bayan an kama Minsitan albarkatun gona bisa zargin sa da aikata laifin cin hanci da rashawa.

Tuni dai Al-Sisi ya buakci tsohon Minstan albarkatun mai, Sherif Isma’il da ya kafa sabuwar Majalisar Ministoci nanda mako guda.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.