Philippines
Guguwar Koppu ta yi barna a Philippines
Daruruwan mutane ne suka makale a gidajensu a kasar Philippines sakamakon ruwan sama da ya haifar da ambaliya da ta mamaye gidaje da gonaki tare da tafiya da dabbobi.
Wallafawa ranar:
Talla
Mummunar Guguwar Koppu mai tafe da iska ce ta haifar da ambaliyar ruwan.
Ya zuwa yanzu hukumomin kasar sun ce akalla mutane 60,000 suka tserewa gidajensu, don kaucewa bala’in da aka dade ba a ga irinsa ba.
Rahotanni sun ce tuni gwamnatin kasar ta tura sojoji da jami’an kananan hukumomi da kuma masu aikin agaji kauyuka 70 da bala’in ya shafa don gudanar da aikin agaji.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu