Isa ga babban shafi
Afghanistan

Taliban ta kashe Sojojin Amurka 6 a Afghanistan

Wani Dan kungiyar Taliban akan babur ya kashe sojojin Amurka guda shida a wani harin kunar bakin waken da ya kai musu a kusa da birnin Kabul da ke kasar Afghanistan.

Afghhanistan na fama da hare haren mayakan Taliban
Afghhanistan na fama da hare haren mayakan Taliban REUTERS/Ahmad Masood
Talla

Rahotanni sun ce an kai harin ne lokacin da sojojin tare da wasu na Afghanistan ke sintirin hadin gwiwa, kuma tuni kungiyar Taliban ta dauki alhakin kai harin.

Harin na zuwa ne a dai dai lokacin da mayakan kungiyar ke kama garin Helmand inda gwamnan Yankin ya ce Taliban ta kama cibiyar ‘Yan Sandan garin da ofishin gwamna da kuma gine-ginen gwamnati.

Kame garin Helmand dai babban kalubale ne ga Sojojin Afghanistan wadanda ke jan ragamar tafiyar da tsaro a kasar bayan ficewa dakarun NATO.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.