Isa ga babban shafi
Saudiya

Gobara ta hallaka mutane a asibitin Saudiya

Hukumomin Saudiya sun bayyana cewa wata gobara da ta tashi a wani babban asbiti da ke yankin kudancin kasar ta hallaka mutane 25 tare da jikkata 107.

Mutane 25 sun hallaka a gobarar da ta tashi a asibitin Jazan na Saudiya.
Mutane 25 sun hallaka a gobarar da ta tashi a asibitin Jazan na Saudiya. news.yahoo.com
Talla

Tuni dai aka yi nasarar kashe gobarar wadda ta tashi a sahsen kula da mata masu juna biyu na asibitin Jazan kuma jami’an tsaro ne suka taimaka wajen kashe ta.

Al-ummar kasar na tofa albarkacin bakinsu dangane da tashin gobarar, inda wasu daga cikinsu suka caccaki hukumomin kasar a shafukan sada zumunta na internet sakamakon rashin kula da asibitin.

Wasu kuwa sun bukaci a sauke minitan lafiya na kasar Khalid al-Falih daga kujerarsa.

A watan Agustan da ta gabata mutane 10 sun rasa rayukansu yayinda sama da 200 suka jikkata sakamakon hatsarin gobara a wani babban gini da kamfanin man fetur na Aramco ke amfani da shi a yankin gabashin kasar.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.