Gada ta kashe mutane 25 a India
Rahotanni daga kasar India na cewa, kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 25 da suka rasa rayukansu sakamakon faduwar wata gada mai tsawon mita 100 a yankin gabashin kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Jami'an agaji sun shafe daren da ya gabata suna kokarin lalubo wadanda suka makale a karkashin gadar yayin da suka bayyana cewa, mawuyaci ne a sake samun wanda ya tsira da ransa.
A jiya Alhamis ne gadar wadda ake ginawa a Kolkata ta fado akan jama'ar da ke hada-hada kamar yadda suka saba yau da kullum, inda ta jikkata mutane kusan 100 baya ga ga kisan da ta yi.
To sai dai har yanzu an gaza gano musabbabin rubtawar gadar yayin da jami'an ceto kusan 300 su ka ci gaba da kokarin neman wadanda gadar ta danne duk da cewa an debe tsammanin samun mutun guda da rai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu