Isa ga babban shafi
Syria

IS ta sake shiga birnin Palmyra na Syria

Mayakan kungiyar IS sun sake shiga birnin Palmyra wanda da dakarun Syria suka fatattake su daga cikinsa watanni takwas da suka gabata.

Birnin Palmyra na Syria
Birnin Palmyra na Syria 路透社
Talla

Kungiyar da ke sa ido kan hakkin dan Adam a Syria ta ce, a halin yanzu mayakan sun mamaye yankin arewa maso yammacin birnin, in da kuma suke gwabza yaki da sojojin gwamnati.

Birnin dai ya shafe kusan shekara guda a hannun mayakan kafin kwace shi a cikin watan Maris.

Rahotanni sun ce, tuni fararen hula suka fara tururuwan ficewa daga birnin mai dimbin tarihi.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.