Isa ga babban shafi
Turkiya- Amurka

Turkiya ta zargi Amurka da taimakawa mayakan kurdawa YPG

Gwamnatin Turkiya ta zargi rundunar sojin Amurka da taimakawa mayakan kurdawa na YPG, wadanda ke neman yancin ballewar daga yankin kurdawan da ke Turkiya.

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan
Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan REUTERS/Brendan McDermid
Talla

Turkiya dai na kallon Kungiyar YPG a matsayin reshen kungiyar PKK da ta ke dauka a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda.

An dai jima ana kai ruwa rana tsakanin Amurka da Turkiya bisa wannan zargi.

Sai dai a yanzu Turkiya na fatan bayan fara aikin zababben shugaban Amurka Donald Trump, ya janye taimakon da kasar ke bai wa mayakan Kurdawan na YPG da ke da alaka da jam’iyyar adawar kasar ta PYD.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.