Isa ga babban shafi
Iraqi

Mutane 7 sun mutu a zanga-zangar kin jinin gwamnati

Akalla mutane bakwai ne suka rasa rayukansu ciki har da Dansanda guda a arangamar  tsakanin masu zanga-zangar neman gudanar da sauye sauye a hukumar da ke sa ido kan lamurran zabuka da jami’an tsaro a birnin Baghdad na Iraki.

Mutane 7 sun mutu a zanga-zangar kin jinin gwamnati
Mutane 7 sun mutu a zanga-zangar kin jinin gwamnati REUTERS/Thaier Al-Sudani
Talla

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar a yau asabar, baya ga wadanda suka mutu akwai wasu da dama da suka sami rauni kamar yadda wani babban jami’in ‘yansandan kasar ya sanar.

Rahotanni na cewa an jefa wasu rokoki a yankin tsaro na Green zone da ake da ginin majalisar dokokin kasar da ofisoshin jakadancin wasu kasashen Duniya.

Al’amarin ya auku ne a tsakiyar birnin Baghdad.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.