Isa ga babban shafi
Iraq

Yar jarida ta mutu a farmakin kwato Mosul

Rahotanni daga kasar Iraki na cewa wata ‘yar jarida ta rasa ranta a lokacin da take kokarin dauko rahoto a  fadan da ake yi a tsakanin gwamnatin Iraki da mayakan Daesh na ISIL na sake kwato birnin Mosul.

Dakarun sojin Iraki sun kaddamar da farmakin kwato birnin Mosul daga ikon ISIL.
Dakarun sojin Iraki sun kaddamar da farmakin kwato birnin Mosul daga ikon ISIL. REUTERS/Ahmed Saad
Talla

Kafar talabijin Kurdawan Iraki da ‘yar jaridar ke aiki ce ta sanar da mutuwarta.
‘Yar jaridar mai suna Shifa Gardi ta gamu da ajalinta a harin bam a yau asabar.

Ta kuma mutu ne tana da shekaru 30 a Duniya.

A makon da ya gabata ne dakarun sojin Iraki suka kaddamar da farmakin sake kwato birnin Mosul birni na biyu mafi girma a kasar daga ikon mayakan ISIL.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.