Afghanistan
An kai harin bam a masallacin 'yan Shi'a a Kabul
Wasu ‘yan kunar bakin wake sun tada bam a wani Masallachin mabiya mazhabar Shi’a da ke Kabul na kasar Afghanistan, inda suka kashe mutane 4 suka kuma jikkata wasu da dama.
Wallafawa ranar:
Talla
Najib Danish, mai magana da yawun ma’aikatar cikin gidan kasar, ya ce an kai harin ne a Masallachin Al Zahra da ke yammacin birnin na Kabul.
Kungiyar ISIS ta dauki alhakin kai harin, wanda shi ne irinsa na farko da aka kai wa masallacin da mabiya mazhabar ta Shi’a ke ibada cikinsa a wannan wata na Ramadan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu