Isa ga babban shafi
Afghanistan

An kai harin bam a masallacin 'yan Shi'a a Kabul

Wasu ‘yan kunar bakin wake sun tada bam a wani Masallachin mabiya mazhabar Shi’a da ke Kabul na kasar Afghanistan, inda suka kashe mutane 4 suka kuma jikkata wasu da dama.

Wani hari a birni Kabul, Afghanistan cikin watan mayun 2017.
Wani hari a birni Kabul, Afghanistan cikin watan mayun 2017. REUTERS/Omar Sobhani
Talla

Najib Danish, mai magana da yawun ma’aikatar cikin gidan kasar, ya ce an kai harin ne a Masallachin Al Zahra da ke yammacin birnin na Kabul.

Kungiyar ISIS ta dauki alhakin kai harin, wanda shi ne irinsa na farko da aka kai wa masallacin da mabiya mazhabar ta Shi’a ke ibada cikinsa a wannan wata na Ramadan.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.