Isa ga babban shafi
Afghanistan

ISIS ta kai hari a ofishin jakadancin Iraqi a Afghanistan

Jami’an tsaron Afghanistan na dauki-ba-dadi da mayakan ISIS a harabar ofishin jakadancin Iraqi da ke birnin Kabul

Jami'an tsaron Afghanistan da ke fagen-daga da mayakan ISIS a ofishin jakadancin Iraqi a birnin Kabul
Jami'an tsaron Afghanistan da ke fagen-daga da mayakan ISIS a ofishin jakadancin Iraqi a birnin Kabul REUTERS/Mohammad Ismail
Talla

Wannan na zuwa ne bayan wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa a kofar shiga harabar ofishin jakadancin, yayin da wasu mayaka uku suka yi nasarar kutsawa cikin harabar.

Kawo yanzu babu wani bayani game da adadin mutanen da suka rasa rayukansu ko kuma suka jikkata a harin na yau.

An dai kwahe ma’aikatan ofishin jakadancin bayan jami’an tsaron sun kai dauki kamar yadda ma’aikatar harkokin cikin gidan Afghanistan ta sanar.

Bakin hayaki ya turnuke sararin samaniya a binin na Kabul, yayin da ake ci gaba da jin karar jiniyar motocin dauka marasa lafiya da kuma harbe-harben bindiga.

‘Yan ta’adda da suka hada da Taliban sun kai hare-hare da dama a Afghanistan a cikin wannan shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.