Isa ga babban shafi

"Yawan fararen hular da suka hallaka a Syria da Iraqi ya ninka a 2017"

Wata kungiya mai zaman kanta da ke sa ido kan yakin da Amurka ke jagoranta da mayakan IS a kasashen Syria da Iraqi, ta ce yawan fararen hular da rayukansu ke salwanta a dalilin yakin ya karu da kashi 200 a shekarar 2017.

Wasu manyan gine-gine da kungiyoyin kare hakkin dan adam suka zargi sojojin gwamnatin Syria da kai wa hari, a garin Douma da ke makwabtaka da birnin Damascus.
Wasu manyan gine-gine da kungiyoyin kare hakkin dan adam suka zargi sojojin gwamnatin Syria da kai wa hari, a garin Douma da ke makwabtaka da birnin Damascus. REUTERS/Amer Almohibany
Talla

Kungiyar mai suna Airwars, ta ce alkalumman rayukan fararen hlar da suka salwanta, ya zarta na shekarar 2016, inda aka hallaka fararen hula tsakanin 3,923 da kuma dubu 6,102 a kasashen na Iraqi da Syria.

Kungiyar ta daganta karuwar rasa rayukan da yadda a shekarar da ta wuce, mayakan IS suka ja tunga a garuruwa ko birane masu yawan jama’a, musamman a birnin Mosul na Iraqi da kuma Raqqa da ke kasar Syria.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.