Isa ga babban shafi
Syria

Ana kwashe 'yan tawaye da iyalansu daga garuruwan gabashin Ghouta

Mayakan ‘yan tawayen Syria suna ci gaba da ficewa daga garuruwan yankin gabashin Ghouta tare da iyalansu, bayan da sojojin gwamnati suka yi nasarar mamaye mafi akasarin yankin.

Wasu mayakan 'yan tawayen Syria tare da iyalansu yayin da manyan motoci suka fara aikin kwashe su daga yankin gabashin Ghouta.
Wasu mayakan 'yan tawayen Syria tare da iyalansu yayin da manyan motoci suka fara aikin kwashe su daga yankin gabashin Ghouta. AFP
Talla

A daren ranar Asabar jerin gwanon manyan motoci suka fara aikin kwashe mayakan da iyalansu, bayan cinmma yarjejeniya tsakanin ‘yan tawayen da gwamnati.

Zuwa yanzu kusan kashi 90 na yankin gabashin Ghouta yana hannun sojin Syria, birnin Douma kadai ne a halin yanzu yake hannun, ‘yan tawayen.

Rahotanni sun ce suma ‘yan tawayen kungiyar Jaish al-Islam, da ke iko da Douma, suna kan tataunawa da gwamnati, domin mika mata birnin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.